KannywoodLabarai

Kotu Tace a Cigaba Da Tsare Murja a Gidan Gyaran Hali

Kotun shari’ar musulunci mai zaman ta a filin Hoki a jihar Kano, ta bayar da umurnin a cigaba da tsare shahrarriyar ƴar dandalin TikTok, Murja Ibrahim Kunya, a gidan gyaran hali.

Kotun ta bayar da wannan umurnin ne a yau Alhamis, 16 ga watan Febrairu, a yayin da ta cigaba da sauraron ƙarar d ake yiwa Murja bayan ta gurfana a gabanta.

Alƙalin kotun shari’ar musuluncin yayi umurnin a mayar da Murja Ibrahim Kunya gidan gyaran hali da tarbiyya har zuwa nan da mako guda.

Murja dai har ila yau ta musanta tuhumar da ake yi mata a gaban kotu.

Lauyan Murja ya nemi kotu da ta bayar da belin ta, amma lauyan gwamnati ya ƙi yarda da hakan inda ya nemi da a bashi sati guda domin yayi martani.

Kotun ta tura Murja zuwa gidan yari har zuwa 23 ga watan Fabrairun da muke ciki.

Dangane da tuhumar da aka soma yiwa Murja a zaman da ya gabata kuwa, Murja ta rubuto takardar cewa ta tuba.

Kotun ta ce za ta yi nazari a zaman ta na gaba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Shiga WhatsApp Group Din Mu