Kannywood

Kalli Yadda Aka Fara Daukar Sabon Shirin rahama Sadau a Karo na biyu a Kasar India

Kalli Yadda Aka Fara Daukar Sabon Shirin rahama Sadau a Karo na biyu a Kasar India.

An Fara Daukar Sabon Shirin Jaruma rahama Sadau a Karo na biyu a Kasar India Kuma Zata Fito ne tare da Fitaccen Jarumin Bollywood din nan Me Suna RajneeshDuggal

Fitacciyar Jaruma a Masana’antar Kannywood rahama ibrahim da akafi sani da rahama sadau ta Sauka cikin Garin Mumbhai ta kasar indiya inda zata fara Daukar Sabon Shirinta a Karo na biyu.

Ana jitajitar cewa soabon fim din da jarumar zata fara dauka mai suna NOLLYWOOD GOES TO INIDA zata fito ne tare da Fitaccen Jarumin Bollywood din nan me suna RajneeshDuggal Kamar yadda Shafin labaran Kannywood ya wallafa a Shafinsa na Twitter.

Wannan dai ba shine karo na farko ba da jarumar zata fito acikin Finafinan kasar ta india, watannin da suka gabata Jarumar taje har kasar ta indiya inda ta halarci Wurin da ake daukar fitaccen Shirin nan Me suna Khuda Hafiz Kashi na biyu.

Duk da cewa Ba wani nunata da yawa akayi acikin Shirin ba amma hakan ya matukar jawo Hankalin Mutane Kasancewar itace mace ta farko a arewacin Nigeria Musamman ma a Masana’antar Kannywood
data fara fitowa acikin Fim din india.

A wannan karon kuma tayi tafiyar ne tare da Kawarta Wacce suke uwa daya uba daya watau Fatima ibrahim da akafi sani da teemah Sadau.Ga kadan daga cikin Hotunan yadda Daukar Shirin ya fara gudana daga
garin Mumbhai ta kasar indiya.

Zakuji cikakken bayanin ta hanyar danna hoton bidiyo dake kasa:

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Shiga WhatsApp Group Din Mu