Biography / Tarihi

Cikakken Tarihin Nafisa Abdullahi

Nafisat Abdullahi asalin sunan ta shine Nafisat Abdurrahman Abdullahi Amma anfi sanin ta da Nafisa Abdullahi ko Kuma Nafisa Sai Wata Rana. An haife ta a ranar 23 ga watan janairu a shekara ta 1991.

Farkon rayuwa da iyali

An haifi jaruma Nafisat abdullahi a ranar 23 ga watan Janair a shekara ta dubu ɗaya da ɗari Tara da casa’in da buyu 1992. Ta fara karatun ta na secondary a garin Jos Kuma ta karasa a Abuja. A shekarar 2013 an dakatara da ita daga shirin finan kannywood saboda ta karya doka.

Ilimi

Ta karanci theater art a jami,ar Jos, sannan ta karanci ilimin ɗaukan hoto a landan a makarantan ɗaukan hoto dake Birtaniya.

Fim

Nafisat abdullahi ta fara harkar film ne tun lokacin tana yar shekara sha takwas Kuma film din da ya fito da ita shine SAI WATA RANA a shekara ta 2010 a karkashin kamfanin FKD PRODUCTION Wanda Ali Nuhu ya bada umarni.

Ta bayyana a cikin wani najaria film wato Nollywood Mai suna Blood and Heyna Wanda Kenneth Gyang ya bada umarni, tare da Ali Nuhu da Kuma Sadiq Sani Sadiq.

Ta fito a cikin fim din da Aminu saira ya bada umurni wato ‘Ya daga Allah’ da kuma ‘Kalamu wahid’ a shekarar 2014.

Fina finai

  • Labarina Series [4]
  • Sai Wata Rana
  • Toron Giwa
  • Ummi
  • Zango
  • Ya daga Allah
  • Yar Agadez
  • Addini ko Al’Ada
  • Ahlul Kitab
  • Alkawarina
  • Alhaki Kwikwiyo
  • Alhini
  • Allo (film)
  • Auren Tagwaye
  • Baban Sadik
  • Badi Ba Rai
  • Ban Kasheta Ba
  • Blood and Henna
  • Cikin Waye?
  • Dan Almajiri
  • Dan Marayan Zaki
  • Dare
  • Dawo Dawo
  • Farar Saka
  • Fataken Dare
  • Gabar Cikin Gida
  • Haaja
  • Har Abada
  • Jari Hujja
  • Laifin Dadi
  • Lamiraj
  • Madubin Dubawa
  • Guguwar So
  • Baiwar Allah

Lamban girma

Ta samu kyautittikan girmamawa da dama irin su City People Entertainment Award 2013, sannan ta kasance jaruma ta ɗaya a masana’antar Kannywood a shekara ta dubu biyu da sha hudu 2014. Jarumar ta karɓi kautar girmamawa ta.

AMMA award a shekara ta dubu biyu da sha biyar 2015, MTN award a shekara ta dubu biyu da sha shida 2016, da Kuma Afro Hollywood award a shekara ta dubu biyu da sha bakwai 2017. Nafisa Abdullahi tayi soyyaya da Adam Zango har tayi burin aurenshi.

Kucigaba da kasancewa da shafin manuniya mai albarka mungode da ziyara danna almar kararrawa domin samun ingantattun ayyukanmu masu gamsarwa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Shiga WhatsApp Group Din Mu