Labarai

Buhari ne zai jagoranci APC yakin neman zaben Tinubu a Abuja yau

Buhari ya halarci wani gangamin yakin neman zaben Tinubu a jihar Sokoto a farkon makon nan.

Da alama a karshe shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yanke shawarar yiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar sa, Asiwaju Bola Tinubu kamfen, yayin da yake shirin kaddamar da yakin neman zabensa a Abuja a yau Asabar 11 ga watan Fabrairu, 2023.

Wannan ya zo daidai makonni biyu a gudanar da zaben shugaban kasa da aka shirya gudanarwa a ranar 25 ga Fabrairu, 2023.

Idan dai za a iya tunawa, a farkon makon ne Buhari ya raka Tinubu zuwa taron gangamin shugaban kasa na jam’iyyar APC a jihar Sokoto.

Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da wasu bangarori daban daban musamman na babbar jam’iyyar adawa ta PDP ke cewa Buhari bai damu ba musamman ganin tsohon gwamnan jihar Legas ya gaje shi.

Sai dai a wata tattaunawa ta wayar tarho da jaridar The Punch ranar Asabar, kakakin kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, Festus Keyamo, ya tabbatar da cewa shugaban zai halarci taron na Abuja.

Pulse ta ruwaito cewa jam’iyyar APC na gudanar da taro guda biyu a jihohin Kebbi da kuma babban birnin tarayya Abuja a yau.

A halin da ake ciki, Keyamo ya bayyana cewa ana sa ran fara taron na Kebbi daga karfe 11:00 na safe zuwa karfe 1:00 na rana, yayin da za a fara gangamin Abuja daga karfe 2:00 na rana zuwa 5:00 na yamma.

Kalaman Keyamo: “Ban da tabbacin shugaban kasa zai halarci taron na Kebbi, tabbas zai yi kamfen tare da shi a nan Abuja.

“Ban da tabbacin shugaban kasa zai halarci taron na Kebbi, tabbas zai yi kamfen tare da shi a nan Abuja.

“A ranar Lahadi kuma, Tinubu zai yi ganawa da ‘yan kasuwa da sauran kwararru a babban birnin tarayya Abuja. Kuma a ranar Talata zai je jihar Imo domin ci gaba da yakin neman zabensa.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Shiga WhatsApp Group Din Mu