Labarai

‘Yan sanda sun kama shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai, Ado Doguwa a Kano

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kama shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai ta jihar Kano Alhassan Ado Doguwa.

An kama Doguwa ne a filin jirgin sama na Aminu Kano yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Abuja bisa zarginsa da hannu wajen kashe wasu mutane tare da kona sakatariyar jam’iyyar New Nigeria People’s Party, NNPP a yayin zaben shugaban kasa da aka kammala.

Har ila yau, an zarge shi da yin amfani da bindigar sa mai tsari tare da korar mutane da dama.

Doguwa wanda rahotanni suka ce ya jagoranci barayin da suka kona sakatariyar jam’iyyar NNPP, inda akalla mutane biyu suka kone kurmus, a halin yanzu yana sanyaya a cikin sashin binciken manyan laifuka na jihar.

Da take tabbatar da faruwar lamarin, rundunar ‘yan sandan jihar ta bayyana cewa akalla mutane uku ne suka mutu a lokacin da aka kona sakatariyar yakin neman zaben jam’iyyar NNPP da ke unguwar Tudunwada a jihar Kano.

Yayin da mutane biyu suka kone kurmus a lokacin tattara sakamakon zaben majalisar wakilai, wanda Dogunwa ya bayyana cewa ya lashe zaben.

Tun da farko, a lokacin da yake jawabi ga ‘yan jarida kafin a kama shi, Dogunwa ya musanta cewa yana da hannu a ciki, ya kuma bayyana cewa har yanzu bai samu wata gayyata ta ‘yan sanda ba.

Dogunwa ya ce, “Ban taba rike bindiga ba. Ban ma san yadda ake rike da bindiga ba. Haka kuma ban taba rike wani makami ba a duk lokacin zaben.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Shiga WhatsApp Group Din Mu