Biography / Tarihi

Cikakken Tarihin Jamila Nagudu

Jamila Umar Nagudu (an haife ta 10 ga Agusta 1985) ƴar wasan Kannywood ce ta Najeriya.

Rayuwar farko da ilimi

An haifi Jamila Nagudu a ranar 10 ga Agusta 1985 a cikin Magana Gumau, ƙaramar hukumar Toro a jihar Bauchi, Najeriya . Jamila ta yi makarantun firamare da sakandare a jihar Bauchi.[ana buƙatar hujja]

Sana’a

Jamila Umar wacce aka fi sani da Jamila Umar Nagudu ta fara fitowa a masana’antar Kannywood a shekarar 2002.

Tun lokacin da ta rabu, ta yanke shawarar fara fim. Ta bar Bauchi ta koma Kano ta gane cewa ta cimma burinta na zama jarumar fina-finai a masana’antar Kannywood. Ta kasance a harkar fim a matsayin mai rawa tun (2002).

Sannan daga baya ta shiga harkar fim kaɗan kaɗan. Ƙoƙarin da ta yi a harkar nishadantarwa da wasan kwaikwayo ya jawo hankalin daraktoci har suka fara nuna ta a cikin fina-finansu. Jamila na iya fitowa a kowace rawa.

Ta fito a fina-finan soyayya amma wani lokacin ma tana fitowa a fina-finan barkwanci. Nagudu ta yi fice sosai a Kannywood ta yadda ake yi mata lakabi da “Sarauniyar Kannywood”. Darakta Aminu Saira shi ne ya fara jefa ta a fim din “Jamila da Jamilu” a matsayin jaruma.[3] An zabe ta a matsayin mafi kyawun Nollywood a Abeokuta.

Rayuwa ta sirri

Jalima ta rabu kuma tana da ɗa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button
Shiga WhatsApp Group Din Mu