Jiragen yakin sojin Nigeria sun tarwatsa sabuwar hedikwatar Boko Haram a Borno
Sojojin saman Nigeria sun kai hari tare da tarwatsa wani sabon sansanin yan Boko Haram a garin Mana Waji dake jihar Borno,
Manuniya ta ruwaito mayakan na yin amafani da sabon sansanin nasu wajen shirya kai hare-hare sannan a wajen ne suke ajiye manyan makamansu
A harin da sojojin suka kai ranar Juma’a sun kashe mayakan Boko Haram da dama kana kuma sun lalata makamansu