Labarai
Gwamnan jihar Lagos, Babajide Sanwo-Olu, ya kamu da cutar korona

A wata sanarwa da ministan lafiya na jihar Lagos, Akin Abayomi, ya fitar a yau Asabar ya ce Gwamnan ya killace kansa tun ranar Juma’a bayan da ya yi hulda da wani mai dauke da cutar
Ya ce a sakamakon gwajin da Gwamnan yayi a jiya Juma’a wanda sakamakon Gwajin ya fito yau Asabar ya nuna Gwamna ya kamu amma suna sa rai zai warke nan bada jimawa ba